Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, jaridar darul-khalij ta habarta cewa, cibiyoyin addinin muslunci na birnin Sharja a kasar hadaddiyar daular larabawa sun fara gudanar da harkokin da suka saba gudanarwa na kur'ani a cikin kowane watan Ramadan mai alfarma tun daga ranar farko da watan mai alfarma.
A kowace shekara musulmin kasar haddaiyar daular larabawa suna gudanar da taruka na karatun kur'ani mai tsarki a masallatai da sauran cibiyoyin addinin muslunci, da ke samun halartar dubban mutane.
631121