IQNA

Isra’ila Ita ce Mai Amfana Da Rikicin Sunnah Da Shi’a Kai Tsaye

23:24 - June 06, 2015
Lambar Labari: 3311462
Bangaren kasa da kasa, ministan harkokin wajen kasar Lebanon yay i ishara da cewa haramtacciyar kasar Isra’ila ita ce take amfana da rikicin shi’a sunna a tsakanin al’ummomin larabawa.


Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-nashrah cewa, ministan harkokin wajen kasar Lebanon Jubran Basil ya bayyana cewa haramtacciyar kasar Isra’ila ita ce take amfana da rikicin shi’a sunna a tsakanin al’ummomin larabawa da kuma musulmi.

Ministan na Lebanon ya ce babu batun banbancin mazhaba a cikin batun yaki da ta’addanci, kuma hankoron da wasu suke yi domin kawo wanann batua  yakin da ake yi da ‘yan ta’adda, hankoro ne kawai na neman samun shia a wajen gwamnatin yahudawan.

Dangane da abin da yake faruwa a cikin kasar ta Lebanon kuwa ministan ya bayyana cewa wajibi ne a kan kowane mutum ya bayar da gudunmawarsa domin tababtar da cewa an yaki yan ta’adda gadan-gadan a duk inda suke  a cikin fadin kasar.

Ya kara da cewa wajibi ne ga duk wani dan kasa na gari ya mara baya ga sojojin kasar ta Lebanon ga kokarin da suke yin a yaki da ‘yan ta’adda, kuma goyon bayan rununar sojin kasar ba goyon bayan wani bangare ba ne, domin kuwa a cikin sojoji a kwai musulmi da dukaknin bangarorinsu, haka nan kuma  akwai kiristoci da dama duk suna aiki tare domin kare kasa.

3311158

Abubuwan Da Ya Shafa: lebanon
captcha