IQNA

Shiri Mai Suna Abin da Ya Faru A Mina Laifin Wane? Daga Talabijin Na Senegal

23:05 - October 20, 2015
Lambar Labari: 3390911
Bangaren kasa da kasa, a matsayin nuna takaici da yin Allawadai da abin da ya faru a Mina an watsa shiri mai suna wake da laifin abin da ya faru a Hajji 2015? A gidana talabijin na Senegal.


Kamfanin dillancin labaran Iqna ya harbata cewa, tashar talabijin ta LAMPE FALL a kasar Senegal da ke da alaka da masu bin tafarkin dariku a kasar, ta yi Allawadai da abin da ya faru a Hajji 2015 ta hanyar watsa wani shiri kan hakan.

An watsa wannan shiri ne kai tsaye daga karfe 16 zuwa 17 na yamma, tare da halartar Sharif Mbalo, shugaban cibiyar Al-yasin ta kasar Senegal, Muhammad Baru wani dan jarida, Sheikh Huna Fay daya dag acikin daraktocin hukumar alhazai ta kasar Senegal, Abdullah Babading daya daga cikin fitattun marubuta na kasar.

Wadanda suka halarci wannan shiri musamman Sharif Mbalo wanda daya ne daga cikin mabiya tafarkin Ahlul bait (AS) a kasar, sun nuna takaici matuka dangane da abin da ya faru da mahajjata  awannan shekara ta hanyar yin aikin da ya zubar da mutuncin masu daukar bakuncin wannan ibada mai girma.

3390504

Abubuwan Da Ya Shafa: senegal
captcha