Kamfanin dillancin labaran Iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na Ma’a cewa, Sheikh Muhammad Hssain babban mai bayar da fatawa a birnin Quds, kuma shugaban majalisar malaman Palastine ya yi gargadi dangane da yada wani kr’ani da aka buga da kura-kurai a cikin bugunsa ta hanyar share wasu ayoyi ko kuma maimaita wasu.
Ya ce an buda wadannan kwafi-kwafi na kur’ani mai tsarki ne a madaba’antar darul bayan da suke dauke da kure.
Shugaban majalisar malaman Palastine y ace akwai wadannan kura kurai ne a cikin shafi na 322, inda aka maimaita su, sai kuma acikin surat Ra’ad inda a nan ma an yi wasu kura-kuran da ya kamata a ce an yi la’akari da su.
Sheikh Muhammad Hussain ya yi kira ga dukaknin mutanen da suka samu wadannan kur’anai, da kuma cibiyoyi na addini da aka raba musu da su tattara su a kawo su cibiyar da ke kula da bayar da fatawa, domin kada a yi amfani da su a cikin kure.
Daga karshe ya ce ya zama wajibi ga cibiyoyi da kuma madaba’antu da suke buga kur’ani mai tsarki da su rika sa lura yadda ya kamata.
3443766