
Kamfanin dillancin labaran iqna ya
habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Alwafd cewa, Shauki
Allam babban mufti na kasar Masar ya bayyana cewa addinin muslunci yana kare hakkokin
dukkanin yan adam ne, domin kuwa a kowane lokaci muslunci yana kallon mutum ne
a matsayinsa na dan adam a matakin
farko.
Ya ci gaba da cewa babu ta’assubanci
a cikin addinin muslunci, a kowane lokaci musulunci yana nan kan matsayinsa na
girmama dan adam da mahangarsa da kuma kiyaye hakkokinsa.
Kamar yadda ya yi ishara da cewa
muslunci yana kallon mutum a matsayin
bil adama, wanda yake da hakkoki na musamman, kuma koda baya yana kan akida ta
muslunci ba ne, dole ne a kiyaye hakkokinsa da kare lafiyarsa, kamar yadda
hakan yake a cikin koyarwar wannan addini mai girma.
Ya kara da cewa wadanda ba musulmi
ba ne da suke rayuwa a kasashen musulmi sheda ne kan hakan, domin kuwa ana
kiyaye hakkokinsu ba tare da cutar da sub a.
Majdi Ashur daya daga cikin wadanda
suke halartar taron a maroko inda aka gabatar da wannan jawabi, shi ma daga
kasar ta Masar ya bayyana cewa, wadanda suke rayuwa akasar Masar sun san yadda wadanda ba musulmi
ba suke rayuwa a cikin yancinsu.
Wannan taro na kasa da kasa an fara
gdanar da shi ne a jiya, domin tattauna hanyoyin ci gaba da kare hakkokin
marassa rinjaye a cikin kasashen musulmi.