IQNA

Zaman Ministocin Harkokin Ilimi Na Kasashen Musulmi A Mali

22:21 - May 01, 2016
Lambar Labari: 3480369
Bangaren kasa da kasa, ministocin harkokin ilimi na kasashen musulmi za su gudanar da zamansu na takwas a birnin Bamako na kasar mali.
Kamfanin dillanicn labaran iqn aya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Iina cewa, Abubakar Keita shugaban kasar ta Mali ne zai jagoranci gudanar da zaman taron.

Bayanin ya ci gaba da cewa, run a ranar Juma’a da ta gabata ce aka cimma wannan yarjejeniya ta gudanar da wannan zaman taro a birnmin Bamako, tsakanin mataimakin babban sakataren kungiyar ISESCO da kuma ministan ilimi na kasar Mali.

Wannan shiri dai kungiyar bunkasa harkokin ilimi da ala’adu ta kasashen msuulmi c eke daukar nauyin shirya shi tsawon shekaru kimanin twakwa s ke nan a jere, inda suke tattauna muhimman batutuwa da suka shafi yanayin ilimi da al’adu da suka shafi musulmi.

Yanzu haka dai jami’an kungiyar ta Isesco sun yi rangadi a kasar ta Mali domin duba wuraren da za a gudanar da taron, da kuma wuraren ajiye baki, inda suka nuna gamsuwarsu da shirin da gwamnatin Mali ta yi.

A zaman da ya gudana a shekarun baya an gudaanar da shi a Saudiya, Libya, Kuwait, Azarbaijan, Malaysia, Sudan da kuma Morocco.

Kuma kungiyar tana gudanar da wannan shiri ne karkashin kulawar kungiyar kasashen msuulmi ta duniya.

3493665

captcha