Daya daga cikin wadanda suka shiga cikin tel din tare da kama daki, wanda kuma musulmi ne, ya bayyana cewa ya samu kyauta darduma da kwafin kur’ani a oel din kasantuwar shi musulmi ne.
Ya ce wannan abin mamaki n, domin babu yadda za a yi mutum mai tsananin kiyayya da kyamar musulmi kamar Donald Trump ya yi hakan face da wata manufa da ta daban.
Kamar yadda kuma ya kara da cewa, tun kafin wannan lokacin ya kasance daga cikin mutane wadanda suke kyamar baki ba ma musulmi ba kawai d suke shigowa cikin kasar Amurka, amma daga bisani kiyayyarsa ta fi yawa a kan musulmi, kasantuwar abubuwan ad suke faruwa na ta’addanci inda yake amfani da hakan a matsayin wani makami na siyasa a kan musulmi.
Yanzu dai wannan mataki da Trump ya dauka na raba kur’ani da darduma ga musulmi ya jawo musayar ra’ayoyi a tsakanin Amurka, inda wasu ke ganin cewa ya canja salon siyasarsa ta kin musulmi, yayin da wasu ke ganin cewa yana nan kan bakansa, amma dai tun da ya tafka kure dole ne ya samu wani sabon salo domin yana da bukatar kuri’insu domin ya dare kan kujerar mulki, inda kuma in ya samu mulki su ne farkon wadanda zai fara dandana wa kuda.