Kamfanin dillancin labaran kur’ani
na iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na minsk.icro
cewa, bayan kammala taron karawa juna sani kan marigayi Imam Khomeini (RA)
cibiyar ta Anestito ta tarihi da ke birnin Minsk fadar mulkin Belarus, raba
wasu daga cikin makaloli da aka rubuta dangane da Imam da kuma tunaninsa.
An raba makaloli guda 17 da aka rubuta, wadanda suka kunshi bangarori daban-daban na tunaninsa da ke bayyana yadda yake kallon lamurra ta fskoki da dama a rayuwarsa.
Gungun makalolin da aka mika a wurin sun hada da gabatarwar da Alexendervich shugaban cibiyar ta Anestoti ta tarohi da kuma mohammad Reza Saburi jakadan kasar Iran a Belarus suka rubuta.
Abin tuni a na dai shi ne an fara gudanar da irin wannan taron karawa juna sani ne a lkacin tunawa da rasuwar Imam Khomeini (RA) a ranar 12 ga watan Khordad, wanda kuma kasar ta Belarus na daga cikin wuraren da ake gabatar da irin wanan taro.