IQNA

Matsalar Farashin Mai Ta Yi Tasiri A Aikin Gina Masallatai A Algeria

22:14 - October 09, 2016
Lambar Labari: 3480839
Bangaren kasa da kasa, sakamaon matsalar faduwar farashin mai a kasuwarsa ta duniya aikin ginin masallatai a Algeriya na tafiyar hawainiya.
Kamfanin dillancin labaran ur’ani na iqna ya habarta cwa ya nakalto daga shafin sadarwa na Almisriyun cewa, faduwar farashin mai a kasuwanninsa na duniya ya shafi aikin gina masallatai manya a kasar Algeriya.

Bisa ga wannan rahoto Muhammad Isa ministan kula da ayyukan addini na Algeriya yana cewa, yanayin da ake ciki a kasar na rashin cikar kudaden kasafi ya sanya dole ne a rage wasu daga cikin ayyukan da ake, wanda hakan ya hada har da ginin wasu daga cikin manyan masallatai a lardunan kasar.

A cikin shekara ta 2013 ce dai maia’aikatar kula da harokin addini ta kasar ta fara gudanar da aikin gina manyan masallai a dukkanin manyan biranan kasar, inda kowane masallaci zai dauki masallata akalla dubu 10 a cikinsa.

Ya kara da cewa aikain gina babban masallaci da ake yi a kasar bai samu matsala ba, domin kuwa yanzu ana gab da kammala aikinsa kamar yadda aka tsara, wanda shi ne masallaci na uku mai girma a bayan harami biyu na Makka da masallacin manzo, an kuma fara aikin ginin nasa n tun a cikin shekara ta 2012 ya zuwa yanzu.

Abin tuni a nan dai shi ne, kasar Algeria tana masallatai manya fiye da dubu 15, kuma da dama daga cikin su an gian su ta haynar sadaukarwar al’umma da kudadensu.

3536711


captcha