Kungiyar kare hakkin bil'adama ta musulmi da ke da mazauni a Landan ta fadawa rresstv mai watsa shirye shiryensa da harshen turanci cewa masallacin yana kan layin Zako kusa da babbar kasuwa na kaduna inda yan shia suke taron na tasu'a.
Kafin haka dai gwamnatin jihar kaduna ta haramta kungiyar yan shia ta Islamic movement in Nigeria IMN wacce ake tsare da jagoranta tun kimanin watanni tara da suka gabata ba tare da gurfanar da shi a gaban kuliya ba.
Kungiyar kare hakkin bil'adaman ta ce ta lura da cewa jami'an tsaron sun hada hatta mata da yara da suka yi kokarin ficewa daga masallacin fita.
Kafin wannan lokacin kami’an tsaron sun kame wasu mutane sha biyar da suke kan hanyarsu ta isa wrin da ake gudanar da wadannan taruka na tasu’a a cikin birnin na Kaduna.