IQNA

Dakatar Da Zirga-Zirgar Jiragen Masar Zuwa Umrah

21:15 - October 14, 2016
Lambar Labari: 3480854
Bangaren kasa da kasa, kamfanin zirga-zirgar jiragen sama na Masar ya sanar da dakatar da zuwa umrah a kasar saudiyya har sai abin da hali ya yi.
Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya nakalto daga kamfanin dillancin labarun Anatoly cewa, kamfanonin yawon bude ido na kasar Masar sun sanar a jiya alhamis cewa, sun jingine dukkanin zirga-zirgar masu zuwa umrah, Saudiyya har illa ma sha Allahu sakamakon Karin harajin da aka na dala 533 a kan kowane fasinja kafin ya samu izinin shiga kasar.

Sharif Said matakin na kamfanonin yawon bude-idon na kasar Masar, ya ce; dalilin yin haka shi ne kara kudin fito da kuma na izinin shiga da fice da Saudiyyar ta karawa 'yan kasar waje.

Saudiyyar dai ta kara kudin samun izinin shiga kasar zuwa dalar Amurka dari biyar da talatin da uku.

Masar din dai ta zama kasar farko da ta jingine zirga-zirgar maniyyata zuwa saudiyyar saboda kara kudin samun izinin shiga.

Wannan mataki dai mahukntan na Saudiyya na danganta shi da matakan da suke dauka na kara tado da komadar tattalin arzikin kasar da ke mawuyacin hali.

Sai dai anasu bangaren asana kan harkokin da ke kai da komowa suna ganin cewa, duk da irin mawuyacin halin da tattalin arzikin Saudiyya ke ciki, amma daukar wannan mataki kan masu ziyara daga Masar yana da alaka da siyasa.

A cikin makon da ya gabata ne dai Masar ta kada kuri’a majalisar dinkin duniya da ke mara baya ga daftarin kdirin da maraba da yaki da ta’addanci, lamarin da ya bakanta wa Saudiyya rai matuka, kwanaki biyu bayan haka ta sanar da dakatar da baiwa Masar danyen amn fetur, haka nan kuma ta janye jakadanta.

3537539


captcha