Wanann harin dai ya zo ne kwana baya bayan barazanar da ministan harkokin wajen kasar Saudiyyah ya yi wa gwamnatin Iraki ne dangane da shirin da take da shi na fatattakar 'yan ta'addan wahabiyyah takfiriyya na ISIS daga birnin Mausul da suke iko da shi.
Yanzu haka dai sojojin kasar Iraki fiye da dubu dari da arbain ne suke ci gaba da yi wa birnin nan Mausul kawayanya da nufin tsarkakae shi daga 'yan ta'addan wahabiyyah takfiriyya na ISIS, lamarin da ya daga hankulan gwamnatocin da ke daukar nauyinsu, musamman Amurka, Saudiyya da kuma turkiya da kawayensu.