Taron wanda za a gudanar a cikin mako mai kamawa, zai samu halartar masana da kuma malamai daga sassa na kasar, kamar yadda zai samu halaratr wasu daga cikin masana na kasar Iran, wadanda za su bayyana mahangarsu dangane da kiran da Imam Khomein (RA) ya yi na wajabcin hada kai tsakanin musulmi, domin tunkarar abubuwan da suke a matsayin kalubale a gare su.
A nasa bangaren babban shehin darikar Muridiyyah wanda ya rubuta littafin tafsirin kur'ani mafi girma a Senegal Sheikh Ahmad Bamba ya sanar da cewa zai samu halartar taron.