IQNA

Kungiyoyin Kasashen Larabawa Da Turai Ba Su Amince Da Ci gaba Da Gina Matsugunan Yahudawa Ba

22:55 - December 21, 2016
Lambar Labari: 3481056
Bangaren kasa da kasa, Ministocin harkokin Wajen na kungiyar tarayyar turai da larabawa suna kin amincewa da gina matsugunan yahudawa yan share wuri zauna.

Kamfanin dilalncin labaran kur'ani na iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga wam cewa, Ministocin harkokin Wajen na kungiyar tarayyar turai da larabawa suna kin amincewa da gina matsugunan yahudawa yan share wuri zauna.

Tashar telbijin din Press tv ta ambato majiyar kungiyar hadin kan kasashen larabwa su ka yi taron hadin guiwa da tarayyar turai a birnin alqahira, na Masar, suna bayyana matsugunan yahudawa 'yan share wuri zauna da haramtacciyar kasar ta ke ginawa da cewa sun sabawa doka.

Bugu da kari, kungiyoyin sun bayyana amfani da karfi da Haramtacciyar kasar Isra'ila ta ke yi domin tilastawa palasdinawa matsuguninsu da cewa yana cin karo da dokokin kasa da kasa.

3555705


captcha