Littafin wanda Taufiq Musa ya rubuta, an yi shi ne domin koyar da kananna yara tarihin annabawa, a makarantu, amma bayan gudanar da bincike kan littafin da abin ya kunsa, ma'aikatar addini ta kasar ta ce akwai cin zarafiga manzon Allah a cikin wasu kissoshin.
Yan haka dai an raba dubban kwafi-kwafi na wannan littafi a makarantun islamiyya da dama na kasar gami da wasu cibiyoyin ilimi.
Ministan ya umarci limamai a dukkanin fadin kasar da yi sanarwa domin a hada dukkanin kwafin littafin a tabbatar da an fitar da shi daga hannun jama'a.