IQNA

Malaman bahrain Sun Allawadai Da Halartar Yahudawa A Kasarsu

20:26 - May 10, 2017
Lambar Labari: 3481501
Bangaren kasa da kasa, manyan malaman addinin muslunci na kasar Bahrain sun tir da Allawadai da ziyarar tawagar yahudawan Isr'ila a kasar.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, tashar talabijin ta Almanar ta bayar da rahoton cewa, a cikin bayanai da manyan malamai daban-daban suka fitar a kasar Bahrain, sun kakkasar suka a kan ziyarar da wata tawagar yahudawan Isra'ila ke ke gudanarwa a kasar, wadda masarautar kasar ke daukar bakuncinsu.

Bayanin malaman ya bayyana hakan a matsayin cin amana ga al'ummar musulmi na Palastinu, wadanda yahudawan Isra'ila ke yi wa kisan gilla a kullum rana ta Allah, tare da kiran masarautar kasar da ta sake yin nazari a hankoronta na kulla kawance da Isra'ila.

Su a nasu bangaren dubban jama'a da suke gudanar da zaman dirshan a kofar gidan babban malamin addini na kasar Ayatollah Isa Kasim, sun yi ta rera taken yin Allawadai da karbar bakuncin tawagar yahudawan Isar'ila da masarautar kasar Bahrain ta yi, tare da bayyana haka a matsin babban cin amana ga al'ummar Palastinu da ma sauran musulmi da larabawa.

3598097


captcha