IQNA

Akalla Mutane Uku Sun rasu A Wani Hari A Kasar Kamaru

17:44 - July 01, 2017
Lambar Labari: 3481660
Bangaren kasa da kasa, akalla mutane uku ne aka tabbatar da rasuwarsu a wani harin kunar bakin wake da aka kaddamar a wani masallaci a arewacin kasar Kamaru.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, an kaddamar da harin ne da asubahin yau a lokacin sallar asuba, inda wasu 'yan mata biyu da suka daura bama-bamai ska shiga masallaci, amma an farga da su kafin shiga masallacin, a nan take suka tarwatsa kansu.

Wani jami'in tsaro ya bayyana cewa, dukkanin 'yan matan biyu sun mutu, sun kuma kashe wasu da suka hada da masu salla da kuma mai gadi.

Jami'in ya kara da cewa, ba a wuce mako guda ba tare da 'yan ta'addan Boko haram sun kaddamar da hare-hare makamanta irin wannan ba, da hakan ya hada da masallatai da kuma wuraren tarukan jama'a kamar kasuwanni da sauransu.

Daga watan June da ya gabata na wanann shekara ta 2017 ya zuwa yanzu mutane 20 ne suka rasu sakamakon irin wadannan hare-hare na ta'addanci.

Wani rahoton majalisar dinkin duniya ya tabbatar da cewa, tun daga lokacin da 'yan ta'addan suka fara kaddamar da irin wadannan hare-hare ya zuwa yanzu sama da mutane miliyan 26 ne suka kaurace ma yankunansu a cikin cikin kasashen da ke makwabtaka da tafkin Chadi.

3614090


captcha