Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta
cewa, a jiya an gudanar da wani zaman taron mabiya addinai a wata majami'ar protestant
a birnin Acra na kasar Ghana tare da halartar malamai daga bangarorin msuulmi
da kiristoci.
Bayanin ya ci gaba da cewa wannan zaman taron shi ne karo na tara da ake gudanar da shi, inda mataimakin babban limamain kasar Ghana ya kasance a wurin tare da wasu malaman kiristoci.
Sheikh Armayau Shu'aibu shi ne mataimakin babban limamin kasar ta Ghana, a lokacin da yake gabatar da jawabi ya bayyana cewa, gudanar da irin wannan taro yana da muhimmanci domin kara kusanto da fahimta a tsakanin mabiya addinai.
Kamar yadda su ma a nasu bangaren malaman addinin kirista sun bayyana musulmi a matsayin 'yan uwansu, wadanda suke 'yan kasa guda kuma suke rayuwa tare.
Dukkanin bangarorin biyu sun jaddada wajabcin yin aiki tukuru a tsakanin malaman addinai na kiristanci da musulmi wajen wayar da kan mabiyansu kan muhimamncin zaman lafiya da hakuri da juna, da kuma girma juna.