IQNA

Karamin Yaro Makaho Ya Lashe Gasar Hardar Kur'ani Ta Masar

16:50 - November 22, 2017
Lambar Labari: 3482124
Bangaren kasa da kasa, Abdulrahman Mahdi Khalil wani karamin yaro ne makaho wanda ya lashe babbar gasar hardar kur'ani ta kasa baki daya a Masar.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Abdulrahman Mahdi Khalil wani karamin yaro ne kuma makaho wanda ya shiga babbar gasar hardar kur'ani ta kasa baki daya a Masar, kuma ya lashe inda ya zo a matsayi na daya.

Wanann yaro dai ya yana yin karatunsa ne bisa salo irin na Mahmud Husri, inda ya samu tarbiya karatun kur'ani a wurin mahaifansa da kuma makarantar da yake zuwa.

Yanzu haka dai yana karatu ne a makarantar firamare a gundumar Manufiyya da ke cikin kasar ta Masar.

Manyan cibiyoyi da suka hada da bababr cibiyar Azahar sun girmama wanann karamin yaro da Allah ya yi masa baiwa ta musamman, da kuma kaifin basira maras misiltuwa, inda lashe gasar hardar kur'ani ta kasa baki daya a Masar, duk kuwa da larurar rashin gani da yake fama da ita.

3665871


captcha