IQNA

Ana Ci Gaba Da Gargadin Mahukuntan Bahrain Kan Rayuwar Ayatollah Isa Kasim

16:51 - November 28, 2017
Lambar Labari: 3482146
Bangaren kasa da kasa, kungiyoyin kare hakkin bil adama a ciki da wajen Bahrain sun gargadi mahukuntan masarauatr kama karya ta Bahrain kan rayuwar Ayatollah Isa Kasim.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, Kungiyar kare hakkokin bil'adama ta kasa da kasa Amnesty International ta bukaci gwamnatin kasar Bahrain da ta bari a kai wa shugaban mabiya tafarkin Shi'a na kasar Sheikh Isa Qasim agaji da kulawa ta likita ta gaggawa sakamakon rashin lafiyar da yake fama da shi.

Kungiyar ta Amnesty International ta yi wannan kiran ne cikin wani sako da ta fitar a shafinta na Twitter inda ta ce sakamaon tabarbarewar yanayin lafiyar Sheikh Isa Qasim, ya zama wajibi mahukutan kasar Bahrain su samar da yanayi na gaggawa da zai ba da dama likitoci su gana da Shehin malamin don yi masa magani.

A shekaran jiya Lahadi ne dai wasu majiyoyi suka bayyana cewar Sheikh Isa Qasim din yana fama da tsananin rashin lafiya sakamakon ci gaba da daurin talalan da gwamnatin Bahrain take masa a gidansa da kuma hana ganawa da shi.

Tun a watan Yunin shekara ta 2016 ne dai gwamnatin Bahrain din ta kwace masa shaidar zamansa dan kasar Bahrain sannan kuma jami'an tsaron kasar suka ci gaba da yin kawanya wa gidansa da hana shi fita lamarin da ke ci gaba da sanya rayuwarsa cikin hatsari.

3667551


captcha