IQNA

Wasu Makaranta Matasa Biyu Daga Rasha Suna Halartar Gasar Kur'ani Ta Azhar

22:48 - March 19, 2018
Lambar Labari: 3482489
Wasu Makaranta Matasa Biyu Daga Rasha Suna Halartar Gasar Kur'ani Ta Azhar
Bangaren kasa da kasa, wasu matasa biyu daga kasar Rasha suna halartar gasar kur'ani da cibiyar Azhar ta shirya a Masar.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin yanar gizo na vetogate.con cewa, wadannan matasa musulmi suna halartar dukkanin tarukan gasar da Azhar ta shirya a birane daban-daban na kasar Masar.

Ahmad Junaid shugaban cibiyar shirya gasar kur'ani mai tsarki a jami'ar Azhar ya bayyana a yayin ganawa da wadannan matasa cewa, abin farin ciki ne yadda lamarin kur'ani yake kara samun wurin zama a tsakanin matasa musulmi na Rasha.

Ya kara karfafa gwiwarsu wajen ci gaba da kara bayar da himma wajen lamarin kur'ani da kuma karfafa harshen larabci.

3701247

 

captcha