Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, wata majiyar diflomasiyya a kasar Jordan ta tabbatar da cewa, za a gudanar da zaman nea matsayi na wakilan kasashen larabawa a kungiyar, domin daukar matakai na nuna kin amincewa da wannan danyen aiki da Isra’ila take aikatawa kan al’ummar Palastine.
Rahoton ya kara da cewa, ana sa ran wannan zama zai gudana a yau Lahadi ko kuma a gobe Litinin, kamar dai yadda bangaren Palastinawan suka nemi da a gudanar da zaman.
A wannan zaman dai kasashen larabawan za su bayyana matsayinsu na yin Allah wadai da hare-haren Isra’ila kan yankin Gaza da kuma kisan palastinawa da ta yi a ranar Juma’a a lokacin da suke yin gangamin ranar kasa.
A jiya ma kwamitin tsaron majalisar dinkin duniya ya kasa fitar da wani kudiri na yin Allah wadai da wannan kisan gilla da Isra’ila ta yi Palastinawa, kwamitin ya kasa daukar matakin saboda Amurka taki amincewa da hakan.