Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoto daga wurin gasar kur'ani ta Malaysia cewa, Mukhtar Dehqan yana taka gagarumar rawa a wajen wanann gasa, inda ya karanta ayoyi na 59 da 66 a surat Nisa.
Sayyid Jawad sadat Fatemi da ke jagorantar tawagar Iran a gasar ya bayyana cewa, sun gamsu da yadda Dehqan yake gudanar da karatunsa.
Haka nan kuma Muhammad ali Sabeghi shugaban karamin ofishin jakadancin Iran a Malaysia ya bayyana gamsuwarsa matuka kan yadda wannan makaranci yake gudanar da karatu, ta yadda hatta alkalan wurin sun nuna gamsuwa da yadda karatunsa ke gudana.