IQNA

Hizbullah Za Ta Gudanar Da Tarukan Ranar Quds A Kan Iyaka Da Palastine

23:47 - June 02, 2018
Lambar Labari: 3482717
Bangaren kasa da kasa, kungiyar Hizbullah za ta gudanar da tarukan ranar Quds a yankin Marun Ra’as.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin Almanar cewa, a ranar Juma’a mai zuwa kungiyar Hizbullah ta kasar Lbanon za ta gudanar da tarukan ranar Quds a yankin Marun Ra’as da ke kan iyaka da Palastinu.

Sayyid Hassan Nasrullah babban sakataren kungiyar Hizbullah zai halarci wannan taro.

A kowace ranar Juma’a ta karshen kowane watan Ramadan ana gudanar da tarukan ranar quds a wannan yankin, amma a shekarar bana taron dauki sabon salo.

3719892

 

 

captcha