IQNA

Yahudawan Sahyuniya Sun Kaddamar Da Farmaki Kan Makabartar Annabi Yusuf

23:33 - June 26, 2018
Lambar Labari: 3482788
Bangaren kasa da kasa, da jijjifin safiyar yau ne gungun yahaudawan sahyuniya suka kaddamar da wani farmaki a kan makabartar annabi Yusuf.

 

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, a yau da jijjifin safiya ne gungun yahaudawan sahyuniya suka kaddamar da wani farmaki a kan makabartar annabi Yusuf da ke garin Nablus a gabar yamma da kogin Jordan.

Wannan farmaki dai ya zo ne a daidai lokacin da yahudawan suke shirin shiga wurin, amma matasan Falastinawa suka hana su, amma daga bisani tare da taimakon jami’an tsaron yahudawa, sun afka a cikin wannan wuri mai alfarma.

A kowace shekara yahudawa sukan yi irin wannan ta’annuti a kan wannan wuri mai albarka, inda kabarin annibi Yusuf (AS) yake.

Ko a shekarar da ta gabata ma sun kai irin wannan farmaki kuma suka ci zarafin Falastinawa da suke garin na Balatah a cikin gudumar Nablus, inda suka jikkata mutane da dama.

3725496

 

 

 

 

 

 

 

captcha