IQNA

0:01 - September 02, 2018
Lambar Labari: 3482943

A Yau Ne Ake Gudanar Zaben 'Yan Majalisar Dokoki A Kasar Mauritania

Tun da safiyar yau ne al'ummar kasar Mauritania suka fara kada kuri'unsu domin zabar 'yan majalisar dokokin kasar da kuma na kananan hukumomi.

A Yau Ne Ake Gudanar Zaben 'Yan Majalisar Dokoki A Kasar Mauritania

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, tun da misalin karfe 7 na safiyar yau ne al'ummar kasar Mauritania suka fara kada kuri'unsu domin zabar 'yan majalisar dokokin kasar da kuma shugabannin kananan hukumomi na kasar.

Tun a shekara ta 2013 ce dai aka gudanar da zabe makamancin wannan, duk kuwa da cewa jam'iyyun adawa na kasar sun kaurace wa zaben a wancan lokacin, amma  a wannan karon jam'iyyun adawa sun shiga zaben, wanda hakan ne ya kara wa zaben na wannan karon armashi matuka.

Tun a farkon wannan makon ne masu sanya ido kan zaben suka fara isa kasar, daga bangaren majalisar dinkin duniya da kuma kungiyar tarayyar turai gami da kungiyar tarayyar Afrika.

A tsakiyar shekara ta 2019 mai kamawa ce dai ake sa ran za a gudanar da zaben shugaban kasa a kasar ta Mauritaniya.

3742981

 

 
captcha