IQNA

Rikici A Kasar Sudan Na Ci Gaba Da Kara Kamari

20:06 - December 28, 2018
Lambar Labari: 3483260
Rikici A Kasar Sudan Na Ci Gaba Da Kara Kamari
Ministan watsa labaru na kasar Sudan ya yi watsi da rahoton kungiyar kare hakkin bil adama ta kasa da kasa akan adadin wadanda jami'an tsaro su ka kashe a yayin Zanga-zanga.

Kamfanin dillancin labaran iqna, kafar watsa labaru ta algad ta ambato ministan na watsa labari Bushara Jum'ah Arur yana cewa; Mutane sha tara ne kadai aka kashe, sai kuma dari hudu da shida da su ka jikkata

ministan watsa labarun na Sudan ya zargi masu Zanga-zangar da lalata dukiyar jama''a sannan kuma ya yi watsi da taken da suka riga bayarwa na sauya gwamnatin kasar.

Bushara ya ce; Batun sauya gwamnati yana da fuska ne ta doka, don haka ta hanyar zabe ne kawai za a iya samar da sauyi

Zanga-zangar Sudan ta shiga makwanni na biyu a jere, daruruwan mutane ne su ka fito kan tituna a cikin garuruwa da birane masu yawa na kasar domin nuna kin amincewa da karin farashin kayan masarufi.

Jami'an tsaron kasar sun yi amfani da karfi wajen tarwatsa masu Zanga-zangar.

Hukumar kare hakkin bil'adama ta Amnesty International' ta ce ya zuwa yanzu jami'an tsaron kasar ta Sudan sun kashe mutane sun kai talatin da takwas.

3776285

 

captcha