IQNA

Sojojin Amurka Sun Yi Harbi A Yankin Da Sojojin Syria Suke A Garin Manbij

21:15 - December 29, 2018
Lambar Labari: 3483263
Sojojin Amurka da ke yankiin manbij a rewacin kasar Syria, sun harba bammai masu haske a yankin da sojojin Syria suke a daren jiya.

Kamfanin dillancin labaran iqna, kamfanin Dillancin labaran Sputnik ya bayar da rahoton cewa, a jiya sojojin Amurka sun harba bama-bamai masu haske da ake harbawa cikin samaniya domin haskaka wuri.

Wannan na zuwa ne kwana daya bayan da sojojin Syria suka shiga cikin garin an manbij wanda yakea  arewacin kasar Syria, inda kafin lokacin mayakan Kurdawa da ke samun goyon bayan Amurka ne suke iko da garin, inda bayan sanarwar da Amurka ta bayar kan fara janye dakarunta daga Syria, Kurdawan sun bukaci sojojin Syria su karbi iko da garin.

Kurdawan sun gabatar da wannan bukata ga sojojin Syria ne a ranar Laraba da ta gabata, da nufin takawa Turkiya birki a yunurinta na kaiwa Kurdawa haria  yankin, inda a ranar Alhamis sojojin Syria suka shiga cikin birnin.

Sojin Amurka sun ce sun harba wadannan bama-bamai masu haske ne da nufin kaucewa taho mu gama tsakaninsyu da sojojin Syria, ta yadda za su iya ganin hanya da kuma wuraren da sojojin Syria suke domin kaucewa haduwa da su

3776376

 

captcha