Kamfanin dillancin labaran iqna, Hamidin Abie shi ne mutum na farko da ya fara gudanar da karatu a gasar kur’ani ta kasar Philippines a masallacin blue mosque.
Bayanin ya ci gaba da cewa, wannan gasa tana samun halartar wakilai daga birane 17 na kasar, tare da halartar jami’ai da kuma malamai, gami da jakadan kasar Iran a kasar Philippines Muhammad Jaafar Malik, da kuma wasu daga cikin dilomasiyyar wasu kasashen musulmi a birnin Manila.