IQNA

An kame wasu Mutane 7 A Pakistan Saboda Keta Alfaramar Kur'ani

23:16 - March 29, 2019
Lambar Labari: 3483506
Jami'an kasar Pakistan sun kame wasu mutane su 7 bayan samun su da laifin keta alfarmar kur'ani mai tsarki.

Kamfanin dillancin labaran iqna, Jaridar Daily Mail ta kasar Birtaniya ta bayar da rahoton cewa, an samu mutanen ne da laifin bankawa takardun kur'ani wuta a wata makabarta da ke garin Qusur a kasar ta Pakistan, da nufin keta alfarmar littafin mai tsarki.

bayan da labarin haka ya watsu al'ummar yankin sun fitoa  cikin fushi, inda suka fara lakadawa mutanen 7 duka, amma daga bisani jami'an tsaro sun kwace su, inda kuma kama su da laifin tozarta kur'ani mai tsarki.

Yanzu haka dai mutanen suna tsare, kuma ana sa ran kotu za ta yanke hukucni mai tsananin a kansua  kan aikata wannan laifi.

Bisa dokokin kasar Pakistan tozarta wani abu daga cikin abubuwan girmama na addinin muslucni yana a matsayin baban laifi, wanda ake yanke hukucni mai tsanania  kansa.

3800089

 

captcha