IQNA

An Yi Wa Fursunoni 89 Afuwa A Kasar Masar Albarkacin Watan Ramadan

23:43 - May 06, 2019
Lambar Labari: 3483612
A yau daya ga watan Ramadan mai alfarma a kasar Masar aka yi wa wasu fursunoni afuwa albarkacin shigowar wannan wata mai alfarma.

Kamfanin dilalncin labaran iqna ya habarta cewa, shafin jaridar Al-ahram ya abyar da rahoton cewa, ofishin shugaban kasar Masar ya fitar da sanarwar yin afuwa daga bangaren shugaban kasar ta Masar Abdulfattah Sisi ga mutane 89, wadanda aka saka su wakahi saboda basussuka.

A kowace shekara shugaba Sisi yana yin afuwa ga wani bangare na fursunonin da ake tsare das u a kasar ta Masar bisa dalilai daban-daban.

A cikin shekara ta 2014 ce Abdulfattah Sisi ya kafa wata kungiyar jin kai mai suna Tahya, wadda kan dauki nauyin biyan basussuka na mutanen da suka kasa biyan bashi har aka kai su wakahi.

3809234

 

 

 

 

captcha