IQNA

23:53 - May 13, 2019
Lambar Labari: 3483635

Martanin Kakakin Ma'aikatar Wajen Fashewar Jiragen Ruwa

Bangaren kasa da kasa, Sayyid Abbas Musawyi ya ce, Jamhuriya Musulinci ta Iran, ta nuna damuwa akan farmakin da gangan da aka kaiwa ga wasu jiragen ruwa a tashar ruwan Fujaïra.

Martanin Kakakin Ma'aikatar Wajen Fashewar Jiragen Ruwa

Kamfanin dillancin labaran iqna, Da yake sanar da hakan kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran, Abbas Moussavi, ya ce yana da kyau a gudanar da bincike kan ire iren wadannan al’amuran dake faruwa, saboda hakan babbar barazana ce ga sha’anin tsaro da kuma zurga zurga ta jiragen ruwa a yankin Golf.

Iran dai na mai danganta lamarin da yadda wasu kasashe ke kokarin wargaza tsaron kan ruwa.

A jiya ne dai hadaddiyar daular larabawa, ta tabbatar da cewa an kai wasu ayyuka data danganta dana aika-aika kan wasu jiragen ruwa na ‘yan kasuwa a gabashin Fujairah, saidai ba tare da bayyana wadanda suka aikata hakan ba.

3811053

 

captcha