IQNA

Martanin Iran Ga Faransa Kan Tsoma Baki A Cikin Harkokinta Na Cikin Gida

22:53 - December 29, 2019
Lambar Labari: 3484356
Sayyid Abbas Musawi ya mayar da martani kan tsoma baki da gwamnatin Faransa ta yi a cikin harkokin Iran.

Kamfanin dillancin labaran IQNA, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Sayyid Abbas Musawi ya mayar da kakkausan martani dangane da tsoma baki da gwamnatin Faransa ta yi a cikin harkokin Iran na cikin gida, musamman dangane da kame wata ba’iraniya mai suna Adelkha, wadda ake zarginta da gudanar da ayyukan liken asisri ga kasashen ketare.

Haka nan kuma dangane da batun wani dan kasar Faransa da aka kame a cikin Iran, hakan ya faru ne bayan saunsa da hannu dumu-dumu a cikin yunkurin haifar da matsalar tsaro a cikin kasar ta Iran, kuma lauyansa yana da masaniya kan komai.

Musawi ya kara da cewa, yada karairayi a fagage na siyasa ko kafofin yada labarai, ba zai hana Iran daukar mataki na shari’a a kan wadanann mutane ba.

 

 

https://iqna.ir/fa/news/3867312

 

 

 

 

captcha