IQNA

23:37 - February 06, 2020
Lambar Labari: 3484492

Isra’ila Ta Kai Hare-Hare A Kusa Da Birnin Damascus Na Syria

Isra’ila ta kai hare-hare da makamai masu linzami a kusa da birnin Damascus na Syra, amma makaman kariya na Syria sun kakkabo makaman na Isra’ila.

Isra’ila Ta Kai Hare-Hare A Kusa Da Birnin Damascus Na Syria

Kamfanin dillancin labaran IQNA, gwamnatin Siriya ta sanar da murkushe wani harin makamai masu linzami da mahukuntan yahudawa mamaya na Isra’ila suka kaddamar a cikin daren jiya a wasu sassan kasar.

Kamfanin dilancin labaren kasar, ya rawaito cewa makamman garkuwa kan hare haren sama sun murkushe wasu jerin hare haren makiya a kusa da Damascus babban birnin kasar.

Hare haren an kai su ne kan yankunan al-Kiswah da Marj al-Sultane da Jisr Bagdad, inda wuta kama a daya daga cikin sansanonin sojin gwamnatin Siriyar.

Wannan dai ba shi karon farko ba da Isra’ila da ke kai ire iren wadannan hare hare a Siriya ba, tun bayan barkewar rikicin kasar a cikin shekara ta dubu biyu da sha daya.

 

 

https://iqna.ir/fa/news/3876975

captcha