IQNA

Jamia’n Tsaron Tunisia Sun Damke Wasu ‘Yan Ta’adda

23:39 - July 23, 2020
Lambar Labari: 3485012
Jamia’n Tsaron Tunisia Sun Damke Wasu ‘Yan Ta’adda
Tehran (IQNA) jami’an tsaron kasar Tunisia sun sanar da samun sarar damke wasu ‘yan ta’addan takfiriyya.

Kamfanin dillancin labaran anatoli ya bayar da rahoton cewa, a wani samame da jami’an tsaron kasar Tunisia suka kai a kan wata maboyar  ‘yan ta’addan takfiriyya a kudancin kasar, sun cafke wasu daga cikinsu.

Ma’aikatar harkokin cikin gida a kasar ta Tunisia ta sanar ad cewa, yan ta’addan suna shirin kaddamar da wasu hare-hare a kan wasu yankuna na kasar.

An samu tarin makamai da kuma abubuwa mas fashewa a cikin mabiyar ‘yan ta’adan, gami nau’ion bindgogi daban-daban.

‘Yan ta’addan wadanda suke da alaka da kngiyar daesh, suna shirin kai haren-haren ansu ne a kan wasu wurare na bude ido da ke cikin kasar.

Baya ga Saudiyya, kasar Tunisia ita ce ta biyu wajen yawan ‘yan ta’adda masu da’awar jihadi da suke kai hare-hare a cikin kasar Syria, inda a halin yanzu Turkiya ta kwaso wasunsu daga Syria zuwa Libya domin yaki da dakarn Haftar a kasar.

 

3911685

 

 

Abubuwan Da Ya Shafa: tunisia
captcha