Sarki Nawaf Al-Ahmad Aljabir Al-Sabah ya bayyana haka a ranar yau Alhamsi a lokacin da yake zantawa da Isma’el Haniyya shugaban kungiyar Hamas ta Falasdniya a yankin Gaza ta wayar tarho.
Sarkin ya kara da cewa kasar Kuwait zata ci gaba da muhimmanci ga al-amuran masu muhimmaci na al-ummar Musulmi, musamman al-ummar Falasdinu.
A na shi bangaren shugaban Hamas Isma’ila Haniyya ya yaba wa marigayi sarki Sabah Al-Ahmad Aljabir Assabah saboda tallafin da ya bawa al-amarin falasdinawa a shekarun da suka gabata.
A ranar Talatan da ta gaba ce sarkin ya rasu yana dan shekara 91 a duniya bayan rashin lafiya.
3926661