IQNA

Kuwait Ta Jaddada Matsayinta Na Ci Gaba Da Goyon Bayan Al'ummar Falastinu

23:40 - October 01, 2020
Lambar Labari: 3485236
Tehran (IQNA) Sabon sarkin kasar Kuwait ya bayyana cewa gwamnati da mutanen kasar za su ci gaba da goyon bayan al-ummar Falasdinu.

Sarki Nawaf Al-Ahmad Aljabir Al-Sabah ya bayyana haka a ranar yau Alhamsi a lokacin da yake zantawa da Isma’el Haniyya shugaban kungiyar Hamas ta Falasdniya a yankin Gaza ta wayar tarho.

Sarkin ya kara da cewa kasar Kuwait zata ci gaba da muhimmanci ga al-amuran masu muhimmaci na al-ummar Musulmi, musamman al-ummar Falasdinu.

A na shi bangaren shugaban Hamas Isma’ila Haniyya ya yaba wa marigayi sarki Sabah Al-Ahmad Aljabir Assabah saboda tallafin da ya bawa al-amarin falasdinawa a shekarun da suka gabata.

A ranar Talatan da ta gaba ce sarkin ya rasu yana dan shekara 91 a duniya bayan rashin lafiya.

 

3926661

 

 

captcha