IQNA

Za A Gudanar Da Baje Kolin Kur’ani A Karon Farko A Birnin Nelson Na Kasar New Zealand

14:59 - December 10, 2020
Lambar Labari: 3485447
Tehran (IQNA) ana shirin gudanar da wani taron baje kolin kur’ani mai tsarki a birnin Nelson na kasar New Zealand.

Shafin yada labarai na Stuff ya byar da rahoton cewa, ana shirin gudanar da wani taron baje kolin kur’ani mai tsarki a birnin Nelson na kasar New Zealand a karon farko a wannan birni.

Rahoton yace wannan baje kolin kur’ani mai tsarki an gudanar da shi a birane daban-daban na kasar New Zealand, amma wannan shi ne karon farko a birnin Nelson.

Daya daga cikin manufin gudanar da baje kolin shi ne, gabatar da kwafi-kwafi na kur’ani mai tsarki da aka tarjama a cikin har Mori, wanda shi ne harshen asali na mutanen New Zealand kafin zuwa turawa a kasar.

Wani malamin addini mai suna Mustenser Qamar shi ne wanda yake jagorantar lamarin baje kolin, wanda kuma ya kwashe tsawon shekaru yana gudanar da ayyuka na addini a kasar.

Malamin ya bayyana cewa, mutane da dama a kasar ba su da masaniya  akan addini, amma ta hanyar gudanar da wasu taruka irin wadannan da suke tara jama’a daban-daban, hakan wata dama ce ta yin bayani kan addinin musulunci.

Baya ga haka kuma ya ce suna amsa tambayoyin mutane da suke bukatar sanin wasu abubuwa dangane da addinin muslunci.

3940243

 

 

 

 

captcha