IQNA

Babbar Malama D Ta Assasa Cibiyar Kur'ani Mafi Girma A Kasar Senegal Ta Rasu

23:50 - December 27, 2020
Lambar Labari: 3485499
Tehran (IQNA) Allah ya yi wa Malama Maryam Inyas babbar malamar addinin musulunci a kasar Senegal rasuwa.

Shafin yada labarai na Sahara Media ya bayar da rahoton cewa, Allah ya yi wa Shikhah Maryam Inyas babbar malamar addinin addinin musulunci a kasar Senegal rasuwa bayan kwashe tsawon shekaru tana hidima ga kur'ani da addinin musulunci.

Wannan mata wadda ta shara a fagen yada ilimin kur'ani mai tsarkia  kasar Senegal, ita ce kuma ta gina babbar cibiyar kur'ani mafi girma  akasar, cibiyar da ta yayae dubban dalibai na cikin kasar Senegal da ma kasashen Afirka da dama.

An haife ta a garin Kaulakha na kasar Senegal a shekara ta 1934, mahaifinta shi ne Sheikh Ibrahim Inyas, babban malamin addinin musulunci, kuma jagoran Faila a darikar Tijjaniya, wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen yada addinin musulunci a kasashen yammacin Afirka.

A cikin shekara ta 2984 ne ta kafa babbar cibiyar addinin musulunci ta Sheikh Ibrahim Inyas a birnin Dakar babban birnin kasar Senegal.

آماده// درگذشت مؤسس بزرگترین مرکز قرآنی در سنگال

3943573

 

captcha