IQNA

Allah Ya Yi Wa Fitaccen Malamin Kur'ani A Masar Sheikh Muhammad Abdulhalim Rasuwa

23:55 - June 25, 2021
Lambar Labari: 3486049
Tehran (IQNA) Allah ya yi wa daya daga cikin fitattun makarantan kur'ani a kasar Masar Sheikh Muhamamd Abdulhalim rasuwa.

Shafin yada labarai na Albayan ya bayar da rahoton cewa, Allah ya yi wa daya daga cikin fitattun makarantan kur'ani a kasar Masar Sheikh Muhamamd Abdulhalim rasuwa a jiya.

Sheikh Muhamamd Abdulhalim wanda daya ne daga cikin limaman kasar Masar, kuma fitaccen malamin kur'ani, ya rasu a jiya a asibiti bayan fama da rashin lafiya na wani lokaci.

Da dama daga cikin almajiransa da kuma masu bibiyar shafukan zumunta  akasar Masar, sun sanya karatunsa na kur'ani mai tsarkia  jiya, a matsayin addu'a a gare shi.

3979740

 

 

 

captcha