IQNA

Hukumomin Soji A Myanmar Sun Saki Dan Addinin Buda Mai Tsananin Kin Musulmi Daga Kurkuku

15:20 - September 10, 2021
Lambar Labari: 3486291
Tehran (IQNA) hukumomin soji a kasar Myanmar sun saki malamin addinin buda mai tsananin kin musulmi da ake tsare da shi a gidan kaso.

Jaridar Phompenh Post ta bayar da rahoton cewa, hukumomin soji a kasar Myanmar sun saki malamin addinin buda mai tsananin kin musulmi Ashin Wirathu da ake tsare da shi a gidan kason kasar.

An kame Ashin Wirathu ne an tsare shi a gidan kaso, bisa zarginsa da tunzura jama'a da kuma yin abubuwan da za su iya haifar da tashin hankali.

Gwamnatin ad sojoji suka hambarar a kasar Myanmar ce dai ta kame shi ta jefa shi kurkuku, bayan ya shiga wata zanga-zangar adawa da gwamnati.

Kafin wannan lokacin dai a cikin shekara ta 2017 jagoran mabiya addinin buda a kasar Myanmar ya bayar da umarnin Ashin Wirathu gudanar da duk wasu harkoki na addini a wuraren ibada na 'yan addinin buda, saboda yadda yake tunzura jama'a wajen kin jinin musulmi a kasar.

 

3996391

 

 

 

captcha