Hukomomi masu kula da wurare masu tsarki a kasar Iraki sun bayyana cewa mutane kimani miliyan 16 ne suka sami damar halartar juyayin 40 na shahadar Imam Husain (a) a birnin Karbala.
Bayanin ya ce mutanen sun fito daga kasar ta Iraki da kuma kasashen duniya daban-daban, sannan daga kasar Iran kadai mutane kimani dubu 90 suka sami halartar juyayin, bayan da hukukomin kasar Iraki suka takaita adadin zuwa dubu 60 kacal da farko.
A wani rahoton kuma jami’an tsaro na Hashd Alshaabi na kasar ta Iraki sun bayyana cewa an kammala juyayin arbi’an a kasar ba tare da fuskantar matsalolin tsaro ba .