IQNA

Sarkin Jordan Ya Gana Da Ministan Yaki Na Isra’ila

18:34 - January 06, 2022
Lambar Labari: 3486787
Tehran (IQNA) A wata ganawa da ya yi da ministan yakin Isra’ila Bani Gantz, Sarki Abdallah na biyu na Kasar Jordan ya tattauna batun ci gaba da farfado tuntubar juna tsakanin gwamnatin Falasdinu da gwamnatin yahudawan Isra’il.

A yayin ganawar, Sarki Abdallah ya jaddada wajabcin wanzar da cikakken zaman lafiya a yankunan Palasdinawa, da daukar dukkan matakan da suka dace don samun cikakken zaman lafiya bisa tsarin samar da kasashe biyu masu cin gishin kansu.

Dangantaka tsakanin Jordan da gwamnatin sahyoniyawan a karkashin tsohon Firaminista Benjamin Netanyahu (2009-2010) ta sukurkuce, inda har sarki Abdallah ya bayyana tu a matsayin "mafi muni" a wata ziyara da ya kai Amurka.

Hare-haren da Isra’ila ke ci gaba da kai wa kan Masallacin Al-Aqsa da kuma wuraren ibadar musulmi a Falasdinu, ya haifar da kara tabarbarewar dangantaka a tsakanin bangarorin biyu, bayan da Jordan ta bayyana hakan a matsayin keta hakkin da take da shin a kula wuraren Falasdinawa da ke gabashin birnin Quds, kamar yadda Majalisar Dinkin Duniya ta tababtar da hakan a cikin wani kudiri a shekaru baya.

 

 

4026618

 

captcha