IQNA

Dan wasan Najeriya ya taimaka wajen gina masallaci a Kamaru

22:17 - January 30, 2022
Lambar Labari: 3486884
Tehran (IQNA) Dan wasan tawagar kwallon kafar Najeriya Ahmed Musa ya bayyana goyon bayansa ga gina babban masallacin Garoua a kasar Kamaru.

Ahmed Musa ya bayar da gudummawar dalar Amurka 1,500 ga babban masallacin garin Garoua, kuma mai taimaka wa Musa kan harkokin yada labarai ya tabbatar da hakan a wata hira da jaridar Muslim News.

Masallacin na kusa da sansanin ‘yan wasan Najeriya ne, kuma an yi amfani da shi wajen shirya ‘yan wasan kwallon kafar Najeriya a gasar cin kofin nahiyar Afrika dake gudana a kasar Kamaru.

Za a kashe wadannan kudade ne wajen aikin gyaran  Masallacin. A baya dai Ahmed Musa ya taba zama gwarzon shekara a kafar yada labarai ta Muslim News.

Ahmed Musa (an haife shi a watan Oktoba 14, 1992) ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne na Najeriya wanda ya taka leda a Fanloo (Netherland), CSKA Moscow, Leicester City (Ingila) da Al Nasr a ƙasar Saudiyya.

4032317

 

 

captcha