IQNA

Mambobin Majalisar Ministocin Isra'ila Sun Keta Alfarmar Masallacin Qud Ta Hanyar Kutsa Kai A Cikinsa

22:26 - February 01, 2022
Lambar Labari: 3486895
Tehran (IQNA) A yau ne mambobin majalisar ministocin yahudawan sahyoniya suka shiga cikin masallacin Al-Aqsa inda suka keta alfamar masallacin.

A yau ne mambobin majalisar ministocin yahudawan sahyoniya suka shiga cikin masallacin Al-Aqsa inda suka keta alfamar masallacin, a gefe guda kuma da wasu daga cikin sojojin yahudawan sahyoniya sun kutsa kai cikin gidan wani shahidan Palasdinawa tare da yin barna da rusa wani bangarensa.

Mambobin majalisar ministocin gwamnatin sahyoniyawan 'yan mamaya sun shiga masallacin Al-Aqsa ba bisa ka'ida ba a 'yan sa'oin da suka gabata.

Kawo yanzu dai ba a san dalilin da ya sa wadannan jami'an yahudawan sahyoniya suka zo wurin sallar ba.

A gefe guda kuma da dama daga cikin 'yan yahudawan sahyuniya sun shiga masallacin Al-Aqsa a safiyar yau tare da mara baya bayan sojojin yahudawan sahyuniya inda suka fara gudanar da ibadar Talmud a harabar masallacin.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Falasdinu a yau cewa, sojojin yahudawan sahyoniya kimanin dari da hamsin sun kai hari a sansanin Shafat inda suka fara yi wa  gidan shahid Abu Shakhid kawanya.

A ranar 21 ga watan Nuwamba ne sojojin mamaya suka harbe Abu Shakhid a tsohon yankin birnin Quds.

Tuni dai dakarun da suka mamaye gidan suka fara rusa gidan ta hanyar rusa katangarsa, amma ba a bar su sun lalata gidajen da ke makwabtaka da shi ba.

4033010

 

captcha