Abu Zuhri ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa: "Muna matukar mutunta kalaman ministan harkokin wajen Aljeriya Ramatan Lamara dangane da batun sulhunta Falasdinu."
Ya kara da cewa: Muna goyon bayan rawar da Aljeriya ke takawa wajen kawo karshen bambance-bambancen da ke tsakanin bangarorin Palasdinawa, muna kuma jaddada goyon bayanmu ga wannan kasa ta wannan fanni, tare da dakile daidaita alaka da 'yan mamaya a yankin.
A ranar 22 ga Disamba, 2021, Abu Zuhri ya ba da sanarwar a cikin wani jawabi cewa: Shugaba Abdel Majid Taboun ya zabi mafi kyawun lokacin da zai sanar da yunkurin kungiyoyin Falasdinawa da ke taro a Aljeriya.
Abu Zuhri ya jaddada cewa: Aljeriya ba ta gamsu da take-taken da wasu ke yi na neman halasta ayyukan ta'addancin Isra'ila ba, kamar yadda kuma ta yi kokari a aikace don hana gwamnatin sahyoniyawan shiga kungiyar Tarayyar Afirka.
Shugaban bangaren siyasa na gwagwarmayar Palasdinawa Hamas ya kammala da cewa: muna goyon bayan duk wani yunkuri daga wata kasa domin kare hakkokin al'ummar Falastinu, da kuma kawo karshen zaluncin da suke fuskanta daga yahudawan Isra'ila 'yan mamaya ba.