IQNA

Gwamnatin San'a Ta Zargi Kawancen Saudiyya Da Saba Yarjejeniyar Tsagaita Wuta A Yemen

16:57 - July 07, 2022
Lambar Labari: 3487519
Tehran (IQNA) Yemen ta zargi rundunar mamayar Saudiyya da kokarin kwace iko da lardin Al-Jawf na kasar Yemen saboda arzikin man fetur a yankin.

Jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen Sayyid Abdul-Malik Al-Houthi ya bayyana cewa: Rundunar kawance da take yakar al’ummar Yemen da taimakon maha’inta a halin yanzu ta fi mai da hankali kan neman kwace iko da lardin Al-Jawf da ke yammacin kasar saboda tarin arzikin man fetur da ke yankin.

Sayyid Houthi ya fayyace cewa: Lardin Al-Jawf ya dauki tsawon shekaru yana fuskantar bakar siyasar zalunci tun daga mahukuntan kasar da suka gabata, inda ya janyo al’ummar lardin take fama da matsanancin talauci, amma da an yi amfani da tarin arzikin lardin, da Al-Jawf tana daga cikin sahun farko masu arzikin karkashin kasa da za su farfado da tattalin arzikin kasar ta Yemen.

 

4069164

 

 

captcha