Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, cibiyar muslunci ta Azhar a kasar Turkiyya ta yi Allah wadai da harin ta’addanci da aka kai a yammacin jiya 22 ga watan Nuwamba a birnin Istanbul na kasar Turkiyya.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na Al-Azhar a shafinsa na Facebook cewa: Azhar ta bayyana goyon bayanta ga jamhuriyar Turkiyya a cikin wannan mummunan lamari tare da jaddada cewa kai hari kan fararen hula almundahana ne a doron kasa kuma ya saba wa dukkanin al'amuran addini da na dan Adam.
Al-Azhar ta mika ta'aziyyarta ga al'ummar Turkiyya da kuma iyalan wadanda lamarin ya shafa.
Kasashe da dama sun yi tir da harin ta'addancin da aka kai jiya a titin Esteghlal da ke tsakiyar birnin Istanbul na kasar Turkiyya, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 6 tare da jikkata wasu fiye da 80 na daban.
Ofishin jakadancin Moroko a Istanbul ya sanar a yammacin Lahadin da ta gabata cewa wasu mata 'yan yawon bude ido 'yan kasar Morocco biyu na daga cikin wadanda suka jikkata a wannan ta'addancin.
A sa'i daya kuma, jami'an sashen karamin ofishin jakadancin na ma'aikatar harkokin wajen kasar Turkiyya sun sanar da cewa babu wani dan kasar Iran da ya mutu a harin ta'addancin da aka kai a birnin Istanbul.
Ministan cikin gidan kasar Turkiyya ya kuma sanar da kame wata mata da ta kai harin bam a Istanbul inda ya kira kungiyar ta'adda ta PKK da ke da alhakin fashewar.
Nasser Kanani kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar ya kuma yi Allah wadai da wannan harin ta'addanci.