An watsa faifan bidiyo na karatun “Ahmed Kuzo”, wani makarancin Turkiyya kuma wanda ya lashe gasar kur’ani ta kasa da kasa karo na 20 na kasar Rasha a yanar gizo.

Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa, an fara gasar ne a ranar Juma’ar da ta gabata 27 ga watan Nuwamba tare da halartar ma’abota karatu daga kasashen duniya daban-daban, kuma aka kammala a ranar Lahadi 29 ga watan Nuwamba.
Ahmed Kuzo, malamin addinin Turkiyya kuma makaranci ne ya samu matsayi na daya a gasar, yayin da Abdurrahman Faraj daga Masar ya zo na biyu sannan Seyed Mustafa Hosseini daga Iran ya zo na uku.
A kasa, Za ku iya kallon bidiyon karatun Ahmad Kozo a wannan gasa, wanda ya sa ya samu nasarar zama na daya: