A rahoton kafofin yada labarai na cikin gida na Falastinu, dakarun da suka kai farmakin sun kwashe masu ibada daga harabar Al-Aqsa tare da kora su zuwa waje.
A halin da ake ciki dai sojojin mamaya sun mamaye gidajen mutanen da ke unguwar Bab Hatta da ke birnin Kudus, a daidai lokacin da rikicin ya barke tsakanin mazauna yankin da dakarun.
Haka nan kuma majiyoyin cikin gida sun ruwaito cewa sojojin sun yi barna a gidaje da dama.
Rahotanni sun ce ko a safiyar jiya Lahadi wasu gungun mahara sun kutsa kai cikin harabar Al-Aqsa, inda suka gudanar da al’adunsu na yahudawa a cikin masallacin mai alfarma.