A rahoton cibiyar yada labaran Falasdinu, firaministan Malaysia Anwar Ibrahim ya jaddada a wata hira da ya yi da tashar talabijin ta Aljazeera Mubasher cewa: Sakonmu ga al'ummar Gaza shi ne mu goya musu baya da kuma hakkinsu na kare kasarsu.
Ya ce: Matsalar ba Houthi ba ce, amma matsalar ita ce yaki da Gaza, kuma dole ne a dakatar da wannan yaki domin kawo karshen duk wani tashin hankali da rikici a yankin.
Anwar Ebrahim ya bayyana cewa: Mun duba da hukumomin Masar hanyoyin da za a bi wajen shigar da kayan agajin da ke cikin Gaza ta mashigar Rafah.
Firaministan Malaysia ya jaddada cewa, kamata ya yi kasashen su mayar da hankali kan yadda ake shan wahala a Gaza.
Anwar Ebrahim ya yi nuni da cewa, jami'an tsaron kasar Malaysia suna cikin shiri mafi kololuwa na dakile duk wani hari na kisan gilla kan Falasdinawa a wannan kasa, ya kuma ce: Za mu yi taka tsantsan da duk wani yunkuri na kashe Falasdinawa a Malaysia.